fidelitybank

Ana fargabar ƴan sanda uku sun mutu bayan an buɗe wuta a kan ɗan takarar gwamnan APC na Edo da Philip Shu’aibu

Date:

Ana fargabar ‘yan sanda uku sun mutu bayan wata arangama da wasu da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne a ranar Alhamis a birnin Benin.

Rahotanni na cewa rikicin ya faru ne da rana, jim kadan bayan dan takarar gwamnan jihar Edo na jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebolo da mataimakin gwamnan da aka dawo da su, Phillip Shaibu, sun bar filin jirgin saman Benin daga Abuja.

Yayin da wasu majiyoyi suka ce ‘yan sanda uku sun samu raunuka a harbin bindiga, wasu kuma sun ce ‘yan sanda uku ne suka rasa rayukansu a yayin arangamar.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Edo, Chidi Nwabuzor domin jin ta bakinsa, ya ce suma sun ji labarin a matsayin jita-jita, ya ce da wuri ne rundunar ta yi wani bayani a kai ba tare da bincike ba.

An bayyana cewa, ba a jima ba Okpebholo da Shaibu suka bar filin jirgin, wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba, a cikin wata motar Sienna da aka ajiye a kofar fita daga filin jirgin, sun harbe ayarin motocinsu.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp