fidelitybank

Ana daf da bayyana sakamakon zaben Kenya

Date:

Cibiyar da ake tattara sakamakon zaben kasar Kenya da ke Nairobi, babban birnin kasar ta dauki harama a yayin da hukumar zaben kasar take kammala tsarin sanar da wanda ya lashe zaben shugaban kasar.

A cewar BBC, abubuwa sun kankama a wurin da za a sanar da sakamakon zaben inda wakilan ‘yan takarar shugaban kasa da lauyoyi da kuma jami’an hukumar zabe suka dukufa wajen tantance takardun rubuta sakamakon zaben da aka aiko daga yuankuna daban-daban na kasar.

Ma’aikata suna can suna goge tebura da kujeru wadanda jami’ai suka yi amfani da su.

Kawo yanzu babu kwamishinonin zabe a wurin da za a sanar da zaben, amma rahotanni sun ce watakila suna can suna gudanar da taruka domin fitar da sanarwar karshe ta sakamakon zaben shugaban kasar.

Babban dakin da za a sanar da sakamakon zaben kasar kenya ya kwashe kwanaki da dama cike da hayaniyar jama’a, inda a wasu lokuta akan samu sabani game da tsarin tattara sakamakon zaben, sai dai yanzu abubuwa sun lafa.

An kara matakan tsaro a kofar shiga babban dakin tattara sakamakon zaben.

Kawo yanzu, Mataimakin shugaban kasa William Ruto yana gaban tsohon Firai Minista Raila Odinga – inda ya samu kashi 51% yayin da shi kuma Odinga ya samu kashi 48%, a cewar kafafen watsa labaran kasar.

Dole ne a ranar da sakamakon zaben zuwa ranar 16 ga watan Agusta, kamar yadda dokokin kasar Kenya suka bayyana.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp