Rundunar sojin Najeriya ta ce, ta lura cike da damuwa da kokarin wasu mutane na birkita tunanin jama’a da gangan, ta hanyar yunkurin shafa kashin kaji da jamhuru ga wani babban hafsanta, Manjo Janar Erema Akerejola, kan zargin sayen gida a Amurka da kudaden almudahanar kwangila.
Ta ce ba shakka, an sayi gidan da ake magana kansa a Amurka, amma bisa yarjejeniyar rancen gina gida da ake biya wata-wata, kuma har yanzu matar Manjo Janar Erema Akerejola wadda mazauniyar Amurka ce, tana ci gaba da biya.
Rundunar sojin Najeriya a sanarwar da daraktan hulda da jama’anta Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce kokarin nuna cewa mai gidan asali ya/ta fito ne daga gidan talakawa, wani kokarin kunyata dukkan ‘yan Najeriya ne masu aiki tukuru, wadanda suka tabuka wani abin kirki a rayuwa.
Sanarwar ta ce muhimmin abu ne a lura cewa an nada Janar Erema Akerejola kan mukamin Babban Hafsan Tsara Dabarun Sufuri da Gyare-gyare na rundunar sojin Najeriya ne wata shida da ya wuce, gidan kuma da ake magana kansa, an mallake shi ne shekara 12 a baya.
Ta kalubalanci mutumin da ya buga labarin a jaridar Sahara Reporters ta intanet da cewa bai iya gabatar da wata shaida ba, in ban da kalmomin wata majiya da bai iya bayyana sunanta ba, wadda ga alama a cewar rundunar sojojin Najeriya na cike da hauci, idan ma akwai ta a zahiri.