Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC ta kama wasu mutane 17 da suka rufe shafukan Facebook daban-daban guda 20 na wasu mutane kuma suka yi amfani da su wajen damfarar wasu mutane a jihar Enugu.
Mai shari’a Ibrahim Buba na babbar kotun tarayya mai lamba 1, Enugu, jihar Enugu, ya yanke wa ‘yan damfaran da aka gurfanar da su a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume guda daya da ya shafi aikata laifuka ta internet.
Wadanda aka yanke wa hukuncin sune: Aguoha Ujunwa, Samson Ebuzoeme, Iwuji Kelechi John Kennedy, Onyeanu Kinsley, Emmanuel Udo, Mmesoma Emmanuel, Prosper Chizaram Ugochukwu, Chima Chibuike Kingsley, Nzeadi Chika Camillus, Nwaugu Nzubechi Bethel.