fidelitybank

An ɗaga likafar shugaban ƙasar Chadi bayan ya fatattaki ƴan Boko Haram da kansa

Date:

Majalisar ƙasar Chadi ta ɗaga darajar shugaban ƙasar, Janar Mahamat Deby zuwa muƙamin Field Marshal, wanda shi ne muƙami mafi girma a rundunar sojin ƙasar.

Ƴanmajalisar sun ɗauki wannan matakin ne bayan kaɗa ƙuri’a a ranar Litinin, inda suka ce, “an ɗaga muƙaminsa saboda sadaukawarsa ga ƙasar da ma rundunar soji, da kuma nasarorin da sojoji ke samu a ciki da wajen ƙasar.”

Ƴanmajalisa 160 ne suka kaɗa ƙuri’ar amincewa, biyu suka ƙi amincewa, sannan shida ba su halarci zaman ba.

An daga muƙamin Mahamat Deby ne a bayan ya ƙaddamar da yaƙi da Boko Haram a yankin tafkin Chadi, bayan wani hari da suka kai ga sojojin ƙasar.

An ruwaito cewa shi ne ya jagoranci sojoji zuwa fatattakar ƴan Boko Haram, wanda aka yi mako biyu ana gwabzawa.

Ya karɓi mulki ne daga mahaifinsa Idris Deby Itno, wanda shi ma ya samu muƙamin a shekarar 2020 yana mai shekara 68.

A watan Mayu ne aka zaɓi Mahamat a matsayin shugaban ƙasar Chadi, inda ake tunanin zai bi tafarkin mahaifinsa wajen yin mulki ba sani ba sabo.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp