Gwamnatin tarayya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar kula da ‘yan ci-rani ta duniya (IOM) ta kwashe ‘yan ƙasa 152 da suka maƙale a Libya.
Ofishin jakandancin Najeriya da ke Libya ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai ta hannun jami’in ofishin.
Jami’in ofishin ya ce wannan shi ne karo na uku da gwamnatin Najeriyar da haɗin gwiwar kungiyar kula da ‘yan ci-rani ta duniya suke shiryawa a shekarar 2023.
Lamarin dai ya kai ga kwashe kusan ‘yan ci-ranin Najeriya 500 da suka maƙale a Libya.