Gwamnatin tarayya ta bayyana ƙarin kuɗin makaranta da fiye da kashi 100 ga sabbin ɗaliban da za su shiga makarantun sakandiren gwamnatin tarayya da aka fi sani da ‘Makarantun Unity’ a faɗin ƙasar.
A yanzu iyayen sabbin ɗaliban za su biya kuɗin makaranta naira 100,000 a maimakon 45,000 da suka biya a shekarar da ta gabata.
Ma’aikatar ilimi ta tarayar ƙasar ce ta bayyana haka, cikin wata sanarwa da ta aike wa shugabannin makarantun sakandiren gwamnatin tarayyar.
Sanarwar mai ɗauke da sa hannun daraktar manyan makarantun sakandire ta ma’aikatar Hajiya Binta Abdulƙadir, ta ce iyayen sabbin ɗalibai za su biya naira 100,000 a zangon karatu na farko na wannan shekera.
Sanarwar ta kuma ƙara da cewa sabon ƙarin kuɗin makarantar zai shafi duka sauran ɓangarori da harkokin makarantar, ciki har da kuɗin kayan makaranta, da na litattafan karatu, da na rubutu, da na wasanni da ƙungiyoyi da sauransu.