fidelitybank

An yi wa Otamendi fashi a gidansa

Date:

 

 

 

A safiyar Litinin ne dai rahotanni daga Portugal su ka baiyana cewa ƴan fashi sun shiga gidan tsohon ɗan wasan Man City, Nicolas Otamendi, su ka yi masa fashi.

Otamendi, ɗan ƙasar Argentina wanda yanzu ya ke taka leda a Benfica da ke Portugal, ya gamu da ibtila’in ne bayan kungiyarsa ta doke Famalicao 4-1 a gasar Premeira.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Benfica ta tabbatar da lamarin, inda ta wallafa a shafinta na yanar gizo cewa a safiyar Litinin ne ƴan fashin su ka shiga gidan ɗan wasan.

Ƙungiyar ta ce ƴan fashin sun tursasa Otamendi da ya buɗe ƙofar gidan nasa, inda bayan ya buɗe, sai su ka kutsa ciki, su ka ɗaure hannuwansa da wuyansa sannan su ka cusa kai cikin ɗakin da matarsa da ƴaƴansa ke kwance.

Bayan sun shiga ɗakin, sai su ka yi awon-gaba da sarƙoƙin gwal da kuma agogunan hannu.

Benfica dai ta baiyana cewa ɗan wasan da iyalinsa na cikin ƙoshin lafiya, inda ta ƙara da cewa ƴan sanda sun fara bincike a kan lamarin.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp