fidelitybank

An yi wa Otamendi fashi a gidansa

Date:

 

 

 

A safiyar Litinin ne dai rahotanni daga Portugal su ka baiyana cewa ƴan fashi sun shiga gidan tsohon ɗan wasan Man City, Nicolas Otamendi, su ka yi masa fashi.

Otamendi, ɗan ƙasar Argentina wanda yanzu ya ke taka leda a Benfica da ke Portugal, ya gamu da ibtila’in ne bayan kungiyarsa ta doke Famalicao 4-1 a gasar Premeira.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Benfica ta tabbatar da lamarin, inda ta wallafa a shafinta na yanar gizo cewa a safiyar Litinin ne ƴan fashin su ka shiga gidan ɗan wasan.

Ƙungiyar ta ce ƴan fashin sun tursasa Otamendi da ya buɗe ƙofar gidan nasa, inda bayan ya buɗe, sai su ka kutsa ciki, su ka ɗaure hannuwansa da wuyansa sannan su ka cusa kai cikin ɗakin da matarsa da ƴaƴansa ke kwance.

Bayan sun shiga ɗakin, sai su ka yi awon-gaba da sarƙoƙin gwal da kuma agogunan hannu.

Benfica dai ta baiyana cewa ɗan wasan da iyalinsa na cikin ƙoshin lafiya, inda ta ƙara da cewa ƴan sanda sun fara bincike a kan lamarin.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp