fidelitybank

An yi wa Matata tiyatar gyaran fuska a Netherland amma ta matan komai – Tijjani Babangida

Date:

Tsohon ɗan ƙwallon Najeriya, Tijjani Babangida ya ce matarsa, Maryam Waziri ta rasa idonta guda ɗaya kuma an yi mata tiyatar gyaran fuska a Netherlands.

A ranar 9 ga watan Mayu ne wani mummunan hatsarin mota ya rutsa da Babangida da iyalansa ciki har da ƙaninsa da matarsa da ɗansa mai shekara ɗaya da rabi, a kan hanyar Kaduna zuwa Zaria.

Cikin wata hira da ya yi da tsohuwar ƙungiyarsa ta Ajax Amsterdam a Netherland, Babangida ya ce damuwar da ya shiga ba za ta taɓa gushewa ba.

Maryam Waziri wadda tauraruwa ce a masana’atar shirya fina-finai ta Kannywood, ta auri tsohon ɗan ƙwallon ne a watan Nuwamban 2021.

Ƙaninsa Ibrahim Babangida ya mutu nan take bayan hatsarin, yayin da ƙaramin ɗansa, mai suna Fadil ya rasu kwanaki bayan hatsarin, sannan mai aikin gidansu ta samu karaya a ƙafa.

Tsohon ɗan wasan na Najeriya ya c,e shi ya ji raunuka a ƙafarsa a lokacin hatsarin, don haka ne ya ƙudiri aniyar taimaka wa matar tasa inda ya tafi Netherlands domin ta samu cikakkiyar kulawa.

Ya kuma ce sakamakon yanayin da matar tasa ta shiga ta manta komai na rayuwarta.

“Bayan shafe wata uku a nan Netherlands, na faɗa mata cewa hatsarin ya rutsa da ƙaramin ɗanmu. Daga nan sai ta fara tambayata wai ya sunansa. Ba ta iya tuna komai”, in ji shi.

Babangida ya kuma yaba da irin gudunmowar da abokansa na ƙwallon ƙafa suka ba shi a ƙasar ta Netherlands.

Ya ce sun taimake shi da duk abin d ake buƙata, kuma sun fara gangamin tara masa kuɗi domin daukar ɗawainiyar jinyar matar tasa, wadda ya ce za ta kwashe shekara guda ana yi mata aiki a asibitin.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp