fidelitybank

An yi wa Matata tiyatar gyaran fuska a Netherland amma ta matan komai – Tijjani Babangida

Date:

Tsohon ɗan ƙwallon Najeriya, Tijjani Babangida ya ce matarsa, Maryam Waziri ta rasa idonta guda ɗaya kuma an yi mata tiyatar gyaran fuska a Netherlands.

A ranar 9 ga watan Mayu ne wani mummunan hatsarin mota ya rutsa da Babangida da iyalansa ciki har da ƙaninsa da matarsa da ɗansa mai shekara ɗaya da rabi, a kan hanyar Kaduna zuwa Zaria.

Cikin wata hira da ya yi da tsohuwar ƙungiyarsa ta Ajax Amsterdam a Netherland, Babangida ya ce damuwar da ya shiga ba za ta taɓa gushewa ba.

Maryam Waziri wadda tauraruwa ce a masana’atar shirya fina-finai ta Kannywood, ta auri tsohon ɗan ƙwallon ne a watan Nuwamban 2021.

Ƙaninsa Ibrahim Babangida ya mutu nan take bayan hatsarin, yayin da ƙaramin ɗansa, mai suna Fadil ya rasu kwanaki bayan hatsarin, sannan mai aikin gidansu ta samu karaya a ƙafa.

Tsohon ɗan wasan na Najeriya ya c,e shi ya ji raunuka a ƙafarsa a lokacin hatsarin, don haka ne ya ƙudiri aniyar taimaka wa matar tasa inda ya tafi Netherlands domin ta samu cikakkiyar kulawa.

Ya kuma ce sakamakon yanayin da matar tasa ta shiga ta manta komai na rayuwarta.

“Bayan shafe wata uku a nan Netherlands, na faɗa mata cewa hatsarin ya rutsa da ƙaramin ɗanmu. Daga nan sai ta fara tambayata wai ya sunansa. Ba ta iya tuna komai”, in ji shi.

Babangida ya kuma yaba da irin gudunmowar da abokansa na ƙwallon ƙafa suka ba shi a ƙasar ta Netherlands.

Ya ce sun taimake shi da duk abin d ake buƙata, kuma sun fara gangamin tara masa kuɗi domin daukar ɗawainiyar jinyar matar tasa, wadda ya ce za ta kwashe shekara guda ana yi mata aiki a asibitin.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp