Wasu al’ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin ƴanbindiga da suka addabe su.
Al’ummar garin Bicci da ke yankin ƙaramar hukumar Danmusa sun zauna tare da Ado Aleru da sauran wasu shugabannin ‘yanbindigan akalla goma, kamar yadda kwamishinan tsaro da harakokin cikin gida na jihar Katsina Dakta Nasiru Mu’azu ya shaida wa BBC.
“An zauna da Ado Aleru da Kamilu Buzaru da Dogo Nahali da Wada Jargaba da Dahiru Buzu haka ma da Nagoggo,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, a ɓangaren al’umma akwai limamai da ƴankasuwa da shugaban ƙaramar hukumar Danmusa.
Talla
“Ƴanbindigar ne suka zo suka nemi zaman lafiya, don haka ne aka háɗu aka tattauna domin tabbatar da zaman lafiyar,” in kwamishinan tsaron na Katsina.