fidelitybank

An yi jana’izar ‘yan sa kai 63 da ‘yan ta’adda suka kashe a Kebbi

Date:

An gudanar da jana’izar kimanin mutum 60 da suka rasa rayukansu sanadiyyar wani harin kwanton ɓauna da ƴan bindiga suka kai wa ƴan sa kai a yankin Zuru da ke cikin jihar Kebbi.

A yammacin ranar Lahadi ne ƴan bindigar suka auka wa ƴan sa kan a kusa da Zirin Daji.

Lamarin ya faru ne a wasu garuruwa na jihar Kebbi da ke kusa da iyaka da jihar Neja bayan kwanton ɓaunar da ƴan bindiga suka yi wa ƴan sa kai, lokacin da ƴan sa kan suka rarake su domin ƙwato dukiyar jama’ar da ƴan bindigar suka yi awon gaba da ita.

Dagacin garin Takita na daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, ya kuma ce wa BBC “gaskiya sun musu kwanton ɓauna sun kashe wajen mutum 63.

“Lokacin da suka shigo da fari sun kwashi mutane da dabbobi ana ta ihun ga ɓarayi, to bayan sun wuce sai ƴan sa kan suka bi bayansu don ceto waɗanda suka kwasa.

“To ashe sun yi wa ƴan sa kan kwanton ɓauna sun ɓuya a saman bishiyoyi, da isar ƴan sa kai wajen sai suka buɗe musu wuta suka kashe su sosai.

Ya ce sun tabbatar da adadin waɗanda suka mutun ne bayan kwaso gawarwakinsu don yin jana’iza.

“Ƴan da kan da aka kashe ɗin sun fito ne daga garuruwa daban-daban ciki har da Takita da sauran wasu garuruwan huɗu.

Sai dai ya ce duk da cewa sun samu labarin su ma ɓarayin dajin an kashe wasu daga cikinsu, to ba su da tabbas akan yawan waɗanda aka kashen.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp