Gwamnatin tarayya ta buƙaci a mayar da waɗanda suke jinya sakamakon fashewar tankar man fetur ta Suleja zuwa manyan asibitoci domin a kula da su da kyau.
Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ya fitar bayan ya jagoranci tawagar wakilan gwamnatin tarayya zuwa inda gobarar ta auku, inda ya ce lamarin ya matuƙar ɗaga hankalin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.
Gobarar wadda ta auku a garin Dikko da ke ƙaramar hukumar Gurara a jihar Neja ta yi ajalin mutane sama da 83, sannan wasu na asibiti, a daidai lokacin da ake neman wasu.
Aƙalla mutum 55 da suka samu raunuka a hatsarin na kwance a babban asibitin Suleja da babban asibitin Sabon Wuse da cibiyar kiwon lafiya a matakin farko ne, wanda hakan ya sa ministan ya buƙaci a kwashe su, a sauya musu asibitoci.
A ƙarshe ministan ya ce gwamnatin tarayya ta kafa kwamiti na musamman domin duba musabbabin yawaitar goara a sanadiyar fashewar tanka a Najeriya.