fidelitybank

An yi jana’izar Mutane 83 da su ka ƙone bayan fashewar Tankar mai a Neja

Date:

Gwamnatin tarayya ta buƙaci a mayar da waɗanda suke jinya sakamakon fashewar tankar man fetur ta Suleja zuwa manyan asibitoci domin a kula da su da kyau.

Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ya fitar bayan ya jagoranci tawagar wakilan gwamnatin tarayya zuwa inda gobarar ta auku, inda ya ce lamarin ya matuƙar ɗaga hankalin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.

Gobarar wadda ta auku a garin Dikko da ke ƙaramar hukumar Gurara a jihar Neja ta yi ajalin mutane sama da 83, sannan wasu na asibiti, a daidai lokacin da ake neman wasu.

Aƙalla mutum 55 da suka samu raunuka a hatsarin na kwance a babban asibitin Suleja da babban asibitin Sabon Wuse da cibiyar kiwon lafiya a matakin farko ne, wanda hakan ya sa ministan ya buƙaci a kwashe su, a sauya musu asibitoci.

A ƙarshe ministan ya ce gwamnatin tarayya ta kafa kwamiti na musamman domin duba musabbabin yawaitar goara a sanadiyar fashewar tanka a Najeriya.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp