Iran ta gudanar da jana’izar mutum 60, ciki har da kwamandojin sojinta da masana nukiliya da Isra’ila ta kashe a kwana 12 da suka yi suka gwabza yaƙi.
An gudanar da jana’izar ce ta karramawa, inda aka lulluɓe gawarwakinsu da tutar Iran, sannan dandazon mutane suka halarta sanye da baƙaƙen kaya domin jimami da kuma karrama waɗanda suka rasun.
A farkon makon ne aka kawo ƙarshen yaƙin ta hanyar shiga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ƙasashen biyu bayan Amurka ta shiga tsakani.
Amurka ta kai hare-hare ne a cibiyoyin nukiliyar Iran, inda ta sanar da cewa ta samu nasarar tarwatsa cibiyoyin, waɗanda dama a kansu ake yaƙin.
Daga cikin waɗanda aka binne akwai Mohammed Bagheri, wanda babban hafsan soji ne a ƙasar ta Iran, kuma shugaban ma’aikata a rundunar sojin ƙasar.
Akwai kuma Hossein Salami, wanda kwamandan dakarun juyin juya-hali ne na Iran, da masanin nukiliyar ƙasar Mohammad Mehdi Tehranchi.
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi mamatan sun sadaukar da kansu domin ƙasar.
Jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei bai samu halartar jana’izar, lamarin da ake dangantawa da barazanar tsaro.