fidelitybank

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Date:

Iran ta gudanar da jana’izar mutum 60, ciki har da kwamandojin sojinta da masana nukiliya da Isra’ila ta kashe a kwana 12 da suka yi suka gwabza yaƙi.

An gudanar da jana’izar ce ta karramawa, inda aka lulluɓe gawarwakinsu da tutar Iran, sannan dandazon mutane suka halarta sanye da baƙaƙen kaya domin jimami da kuma karrama waɗanda suka rasun.

A farkon makon ne aka kawo ƙarshen yaƙin ta hanyar shiga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ƙasashen biyu bayan Amurka ta shiga tsakani.

Amurka ta kai hare-hare ne a cibiyoyin nukiliyar Iran, inda ta sanar da cewa ta samu nasarar tarwatsa cibiyoyin, waɗanda dama a kansu ake yaƙin.

Daga cikin waɗanda aka binne akwai Mohammed Bagheri, wanda babban hafsan soji ne a ƙasar ta Iran, kuma shugaban ma’aikata a rundunar sojin ƙasar.

Akwai kuma Hossein Salami, wanda kwamandan dakarun juyin juya-hali ne na Iran, da masanin nukiliyar ƙasar Mohammad Mehdi Tehranchi.

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi mamatan sun sadaukar da kansu domin ƙasar.

Jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei bai samu halartar jana’izar, lamarin da ake dangantawa da barazanar tsaro.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya...

Mun gano filin wasa na Sani Abacha ba shi da inganci – NPFL

Hukumar shirya gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL),...

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya ya fadi

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinjoji da ya taso daga...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...
X whatsapp