fidelitybank

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Date:

Iran ta gudanar da jana’izar mutum 60, ciki har da kwamandojin sojinta da masana nukiliya da Isra’ila ta kashe a kwana 12 da suka yi suka gwabza yaƙi.

An gudanar da jana’izar ce ta karramawa, inda aka lulluɓe gawarwakinsu da tutar Iran, sannan dandazon mutane suka halarta sanye da baƙaƙen kaya domin jimami da kuma karrama waɗanda suka rasun.

A farkon makon ne aka kawo ƙarshen yaƙin ta hanyar shiga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ƙasashen biyu bayan Amurka ta shiga tsakani.

Amurka ta kai hare-hare ne a cibiyoyin nukiliyar Iran, inda ta sanar da cewa ta samu nasarar tarwatsa cibiyoyin, waɗanda dama a kansu ake yaƙin.

Daga cikin waɗanda aka binne akwai Mohammed Bagheri, wanda babban hafsan soji ne a ƙasar ta Iran, kuma shugaban ma’aikata a rundunar sojin ƙasar.

Akwai kuma Hossein Salami, wanda kwamandan dakarun juyin juya-hali ne na Iran, da masanin nukiliyar ƙasar Mohammad Mehdi Tehranchi.

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi mamatan sun sadaukar da kansu domin ƙasar.

Jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei bai samu halartar jana’izar, lamarin da ake dangantawa da barazanar tsaro.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp