fidelitybank

An yi garkuwa da ɗansanda a Abuja

Date:

Rahotanni na cewa an yi garkuwa da wani ɗansanda mai suna Modestus Ojiebe wanda ke aiki da rundunar ƴansandan jihar Kwara, a babban titin Kubwa da ke cikin birnin.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito daga masanin harkokin ƴanbindinga, Zagazola Makama da ma wasu majiyoyi daga cikin ƴansandan cewa lamarin ya auku ne a kusa da unguwar Dei-Dei gab da barikin ƴansanda da ke Abuja.

“Lamarin ya auku a daidai lokacin da ya tsaya domin ya duba motarsa da ta lalace, sai wasu mutane suka zo a mota, suka ƙwace masa wayoyi da na matarsa. Da suka gane ɗansanda ne sai suka saka shi a motar suka tafi da shi, suka bar matar da motar.”

Sai dai an ce ƴansanda sun baza jami’ansu, domin suke binciken masu wucewa da motoci da zimmar ceto abokin aikin nasu.

Sai dai an yi yunƙurin jin ta bakin kakakin rundunar ƴansandan Abuja, Josephine Adeh, amma haƙar ba ta cimma ruwa ba.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp