Ƴanbindiga sun kai hari a gidan wani mai suna Alhaji Yusha’u Ma’aruf, wanda yake da wani asibiti mai zaman kansa a ƙauyen Zakirai da ka ƙaramar hukumar Gabasawa a jihar Kano.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ƴanbindigar sun yi garkuwa da wani matashi mai shekara 20 mai suna Mohammed Bello, sannan wani ɗan gidan shi mai suna Abubakar ya samu rauni a hannunsa.
Kakakin rundunar ƴansandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce tuni ƴansanda suka fara farautar ɓatagarin domin ceto wanda suka yi garkuwa da shi.
A wani labarin daban, rundunar ƴansandan jihar Kano ta sanar da kama mutum huɗu da take zargin ƴanbindiga ne, sannan ta ƙwace makamai da alburusai da kuɗi kimanin naira 1,028,800.