fidelitybank

An yi garkuwa da wani Likita a jihar Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun yi garkuwa da wani Dakta Mansur Mohammed a jihar Zamfara.

Rahotonni na cewa, an yi garkuwa da jami’an lafiya da wasu da har yanzu ba a tantance adadinsu ba a hanyar Dansadau zuwa Magami a ranar Asabar da ta gabata, 25 ga watan Yuni, 2022.

Kungiyar likitocin Najeriya (NMA) reshen jihar ta tabbatar wa manema labarai hakan a ranar Talata.

Mansur shine Darakta Janar na Babban Asibitin Dansadau.

Da yake bayar da rahoton sace shi, NMA ta yi fatali da yanayin tsaro a jihar, inda ya bukaci gwamnatin tarayya da gwamnatocin Jihohi da su tashi tsaye wajen shawo kan matsalolin da ke damun kasar nan.

Asibitin kamar yadda Daily Post ta ruwaito, ya tabbatar da cewa, an kuma yi garkuwa da fasinjoji da dama a aikin.

Sai dai babu wata sanarwa a hukumance da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar dangane da lamarin.

A halin da ake ciki kuma, a ranar Talata ne gwamnatin jihar Zamfara ta fitar da sharuddan da ya kamata jama’a su samu damar mallakar bindigogi a jihar.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp