fidelitybank

An yi garkuwa da sarki tare da mutane 21 a jihar Taraba

Date:

Rahotanni daga jihar Taraba na cewa an sace mutum 21 har da sarki mai daraja ta uku na al’ummar Pupule, Alhaji Umaru Nyala a ƙaramar hukumar Yorro da ke jihar.

Wasu da ake zargi masu garkuwa da mutane ne suka yi awon gaba da su bayan da suka mamaye ƙauyen cikin dare inda suka riƙa harbin kan mai uwa da wabi a sassa daban-daban na ƙauyen.

Wani shaida da ya yi hira da gidan Talabijin na Channels ya ce cikin mutum 22 da aka sace, har da wata mai juna biyu, da wasu ƴan gida ɗaya da kuma ɗan sarkin da dogarin sarkin.

Wannan ne karo na uku da ake sace mutane don neman kuɗin fansa a ƙauyen cikin ƙasa da wata shida kuma ba a taɓa cafke waɗanda ake zargi ba.

Shaidu sun kuma ce a yanzu, mutanen ƙauyen na zama cikin zullumi yayin da wasu kuma ke tserewa.

Har yanzu ƴan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba inda suka ce sun aike tawagar jami’ansu zuwa wajen domin gudanar da bincike.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp