fidelitybank

An yi garkuwa da mutane 5 bayan sun halarci biki a Anambra

Date:

Akalla mutane biyar ne ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a kauyen Akpo da ke karamar hukumar Aguata ta jihar Anambra a ranar Litinin din da ta gabata.

An rawaito cewa, mutanen da aka sace sun halarci bikin auren wata kawun kwamishiniyar ayyuka na musamman, Sly Ezeokenwa, kuma suna kan hanyarsu ta dawowa ne aka yi garkuwa da su da bindiga.

Kwamishinan wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce, an yi garkuwa da mutanen ne da misalin karfe 10 na daren ranar Litinin a Akpo kuma ba a tuntubi su ko kuma masu garkuwa da mutanen.

Ya ce, “Abokan dan uwana Sampson Okafor, Chidozie Eze, Franklin Osuuagu, Chijioke Uduba, Benedict Ozoagwu wanda ya ziyarci aurensa na gargajiya a jiya (Litinin) an yi garkuwa da su ne da bindiga da misalin karfe 10 na daren jiya a Udo Village, Akpo Aguata a karamar hukumar kan titin Akpo, Nkpologwu kimanin 300m zuwa Akpo Junction. Har yanzu ba mu kulla wata alaka da wadanda abin ya shafa ba.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Toochukwu Ikenganyia shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya kara da cewa rundunar ta kaddamar da aikin ceto mutanen da aka sace.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp