Akalla mutane biyar ne ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a kauyen Akpo da ke karamar hukumar Aguata ta jihar Anambra a ranar Litinin din da ta gabata.
An rawaito cewa, mutanen da aka sace sun halarci bikin auren wata kawun kwamishiniyar ayyuka na musamman, Sly Ezeokenwa, kuma suna kan hanyarsu ta dawowa ne aka yi garkuwa da su da bindiga.
Kwamishinan wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce, an yi garkuwa da mutanen ne da misalin karfe 10 na daren ranar Litinin a Akpo kuma ba a tuntubi su ko kuma masu garkuwa da mutanen.
Ya ce, “Abokan dan uwana Sampson Okafor, Chidozie Eze, Franklin Osuuagu, Chijioke Uduba, Benedict Ozoagwu wanda ya ziyarci aurensa na gargajiya a jiya (Litinin) an yi garkuwa da su ne da bindiga da misalin karfe 10 na daren jiya a Udo Village, Akpo Aguata a karamar hukumar kan titin Akpo, Nkpologwu kimanin 300m zuwa Akpo Junction. Har yanzu ba mu kulla wata alaka da wadanda abin ya shafa ba.”
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Toochukwu Ikenganyia shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya kara da cewa rundunar ta kaddamar da aikin ceto mutanen da aka sace.