fidelitybank

An yi garkuwa da mutane 11 a jihar Taraba har da ɗan Dagaci

Date:

Akalla mutum 11 ne wasu ’yan bindiga suka sace a kauyen Illela da ke Karamar Hukumar Karim Lamido a Jihar Taraba.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa, da misalin karfe 4:00 na safiyar Alhamis ne ’yan bindigar suka auka wa kauyen, sannan suka sace mutanen, cikin su har da wata tsohuwa mai kimanin shekarar 70 mai suna Zainab Adamu.

Majiyar, ta shaida cewa, tsohuwar ta rasu ne a hannun ’yan bindigar, yayin da biyu daga cikin mutanen da aka sace suka kubuta daga inda aka boye su.

Har ila yau, daga cikin mutanen da aka sace har da ɗan Dagacin garin Zip.

Dagacin, Alhaji Uba, ya shaida cewa, dan nasa mai suna, Buhari na daga cikin mutanen da aka sace a yayin harin.

Sai dai ya ce, har har yanzu ya na hannun wadanda suka sace shi.

Alhaji Uba ya ce, ’yan bindigar dai sun bukaci a biya su kudi har Naira miliyan 70 a matsayin kudin fansa.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, DSP Usman Abdullahi, ya tabbatar da faruwar harin, ko da yake bai yi karin haske a kai ba.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp