fidelitybank

An yi garkuwa da Mai Unguwa da Matarsa tare da kashe guda a Bauchi

Date:

A ranar Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki garin Magamin Kano da ke karamar hukumar Ningi a jihar Bauchi inda suka yi awon gaba da matar da dan gidan mai unguwar Alhaji Bashir Abubakar.

Majiyoyi sun bayyana cewa Abubakar ne babban harin ‘yan bindigar da suka nufi gidansa kai tsaye amma ya tsira.

‘Yan bindigar, wadanda aka ce suna dauke da nagartattun muggan makamai, a cewar majiyoyin, sun harbe mutum guda har lahira.

Wani mazaunin garin kuma ‘yan bindigar sun harbe shi a cinyarsa kuma an kai shi babban asibitin Ningi, inda a yanzu haka yake samun kulawa.

Rahotanni na cewa, ‘yan bindigar sun nufi dajin Ningi ne bayan sun shafe sa’o’i da dama suna gudanar da aikin a kauyen inda suka tafi tare da matar da kuma dan hakimin kauyen.

Lamarin na ranar litinin ya kara yawan hare-hare da sace-sacen mutane a karamar hukumar Ningi, inda rashin tsaro ya sanya mazauna yankin cikin damuwa.

Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, a ‘yan makonnin da suka gabata an yi ta yin garkuwa da mutane a yankin, inda aka yi garkuwa da mutane akalla hudu, wasu biyu kuma suka yi mumunan kashe, tare da jikkata wasu da dama.

Rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun nuna cewa mazauna kauyuka daban-daban da aka kai harin sun biya kudin fansa da bai gaza Naira miliyan 50 ba don ganin an sako mutanensu da aka sace a yayin farmakin.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp