fidelitybank

An yi garkuwa da Mace mai juna Biyu a jihar Bauchi

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, ta tabbatar da sace wata mata mai juna biyu, Rahila Da’u, mai shekaru 25 a kauyen Gizaki da ke unguwar Lusa a karamar hukumar Bogoro a jihar.

Kakakin Rundunar, SP Ahmed Wakil wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Bauchi, ya ce, lamarin ya faru ne a ranar 16 ga watan Yuli.

Ya ce, an kai rahoton faruwar lamarin ne a ofishin ‘yan sanda na Bogoro kuma kwamishinan ‘yan sandan, Umar ya bukaci jami’an da su yi duk mai yiwuwa don ceto wanda abin ya shafa.

Ya kara da cewa, jami’an mu ciki harda Batruan ‘yan sanda, suka jagorantanci ziyarci wurin, inda suka kwato harsasai 5 da babu kowa a ciki da masu garkuwa da mutane suka harba.

Sai dai ya tabbatar da cewa, ‘yan sanda na kan gaba wajen tabbatar da cewa, an ceto wanda abin ya shafa ba tare da wani rauni ba.

A halin da ake ciki, shugaban karamar hukumar Bogoro, Mista Iliya Habila, ya yi kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin al’ummar yankin da su kara sanya ido tare da karfafa hanyoyin tsaro na cikin gida domin dakile kwararar baki zuwa yankunansu.

Ya ce, hakan zai kaucewa afkuwar satar mutane a nan gaba da sauran laifuka.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp