fidelitybank

An yi garkuwa da Mace mai juna 2 a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wata mata mai juna biyu a unguwar Lema da ke Mando daura da makarantar horas da sojoji ta (NDA) da ke Zaria a jihar Kaduna.

An yi garkuwa da wasu mutane bakwai a lokacin da ‘yan bindigan suka shiga gidaje uku da misalin karfe 1:00 na safiyar Lahadi.

Daya daga cikin mazauna unguwar Musa Danladi ya ce dukkansu suna tsoron fita daga gidajensu saboda harbin bindiga.

“Sun zo ne da misalin karfe 1:00 na safe, suka tafi da mazauna garin takwas ciki har da wata mata mai juna biyu da ta zo ziyarar mahaifiyarta da ba ta da lafiya a unguwar. Wannan dai ba shi ne karon farko da ‘yan bindiga za su kai wa al’ummarmu hari ba,” inji shi.

Sauran mazauna yankin sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta kawo musu dauki.

Har yanzu dai gwamnati ba ta ce uffan ba kan lamarin, sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Jalige, ya ce zai ji cikakken bayani game da lamarin, a cewar Daily Trust.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...

Najeriya ba za ta karbi ‘yan ciranin Venezuela ba da Amurka za ta ba mu – Najeriya

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ce ƙasar...

Bafarawa ya kafa sabuwar kungiya

Wasu shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki daga...

An fara shirye-shiryen aikin Hajjin badi a Najeriya

Hukumar Alhazan Najeriya ta fara shirhin aikin hajjin 2026...

Na tsallake rijiya da baya lokacin Goodluck – Shettima

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya ce shi ne...

Ya kamata shugabancin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ƴan Kudu

Ministar al'adu ta Najeriya, Hannatu Musawa ta ce ya...

Rashin abinci mai gina jiki Najeriya ce kan gaba a Afirka ta biyu a duniya

Babbar mai taimaka wa shugaban Najeriya Bola Tinubu kan...
X whatsapp