Wani jirgin sama mai saukar ungulu na Majalisar Dinkin Duniya dauke da fasinjoji takwas, ya shiga hannun kungiyar ta’addanci ta al-Shabaab bayan ya yi saukar gaggawa a yankin da kungiyar ke iko da shi.
Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stephane Dujarric ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, kamar yadda CNN ta ruwaito.
Da take bayyana yadda aka kame jirgin mai saukar ungulu, Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta yi saukar gaggawar ne sakamakon wani lamari na injina a yankin Galmudug na Somaliya, wanda ke karkashin ikon kungiyar ta’addanci da ke da alaka da al-Qaeda, a cewar kamfanin dillancin labaran kasar Somaliya.
A cewar SONNA, fasinjojin ‘yan kasashen waje ne, kuma ana ci gaba da aikin ceto.
Ofishin Taimakawa na Majalisar Dinkin Duniya a Somaliya, UNSOM, ya ce jirgin mai saukar ungulu “yana gudanar da aikin kwashe magunguna ta sama” kuma za a fitar da karin bayani idan ya samu.
Wannan ci gaban na zuwa ne makonni bayan da aka kashe Maalim Ayman, babban jigo a kungiyar ta’addanci ta Al-Shabaab a Somalia da Kenya a ranar 17 ga watan Disamba a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin Somaliya da na Amurka suka kai.