fidelitybank

An yi garkuwa da jirgi mai saukar ungulu na majalisar Duniya

Date:

Wani jirgin sama mai saukar ungulu na Majalisar Dinkin Duniya dauke da fasinjoji takwas, ya shiga hannun kungiyar ta’addanci ta al-Shabaab bayan ya yi saukar gaggawa a yankin da kungiyar ke iko da shi.

Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stephane Dujarric ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, kamar yadda CNN ta ruwaito.

Da take bayyana yadda aka kame jirgin mai saukar ungulu, Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta yi saukar gaggawar ne sakamakon wani lamari na injina a yankin Galmudug na Somaliya, wanda ke karkashin ikon kungiyar ta’addanci da ke da alaka da al-Qaeda, a cewar kamfanin dillancin labaran kasar Somaliya.

A cewar SONNA, fasinjojin ‘yan kasashen waje ne, kuma ana ci gaba da aikin ceto.

Ofishin Taimakawa na Majalisar Dinkin Duniya a Somaliya, UNSOM, ya ce jirgin mai saukar ungulu “yana gudanar da aikin kwashe magunguna ta sama” kuma za a fitar da karin bayani idan ya samu.

Wannan ci gaban na zuwa ne makonni bayan da aka kashe Maalim Ayman, babban jigo a kungiyar ta’addanci ta Al-Shabaab a Somalia da Kenya a ranar 17 ga watan Disamba a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin Somaliya da na Amurka suka kai.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp