An yi garkuwa da wani mutum mai shekara 52 ma’aikacin Jarabawar Yammacin Afirka, WAEC, mai kulawa a karkashin karamar hukumar Iseyin ta jihar Oyo, Sunday Adebayo.
Vanguard ta tattaro cewa, an yi garkuwa da shi a hanyarsa ta zuwa makaranta a Iseyin.
Da yake tabbatar da sace shi da safiyar yau, Oninayin Inayin da ke karamar hukumar Iwajowa, Oba Ayansiji Peter ya ce, duk da cewa, an sake shi da safiyar yau kuma aka hada kai da iyalansa, tun da farko masu garkuwan sun bukaci a biya shi Naira miliyan 100. In ji Vanguard.
“Da farko masu garkuwa da mutane sun nemi Naira miliyan 100. Daga baya sun rage shi zuwa Naira miliyan 15. Kamar yadda a daren jiya muna rokon su Naira miliyan biyu, amma suka ce shi. Na samu waya da safiyar yau daga daya daga cikin ‘yan uwansa cewa, an sake shi. Don haka ban san ko nawa ne dangin suka biya ba.” Sarkin gargajiya ya tabbatar.