fidelitybank

An yi garkuwa da Hakimi tare da Ƙaninsa a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan ta’adda da dama a ranar Juma’a sun mamaye gidajen wani Hakimi mai suna Hashimu tare da kaninsa mai suna Danbalange na Birnin Tsaba a karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara inda suka yi garkuwa da su.

Danbalange, wanda dan jam’iyyar All Progressives Congress ne a yankin, tare da Hakimin, sun kasance a ranar Juma’a da misalin karfe 4:30 na safe, kamar yadda wata majiya ta ce, ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da su daga gidajensu.

A cewar majiyar, wasu gungun ‘yan ta’adda da suka hau kan babura sun yi awon gaba da mutanen a gidajensu da ke yankin Birnin Tsaba.

Majiyar ta kara da cewa, “Harin da aka kaiwa mutanen biyu, wani fitaccen dan ta’adda ne ya kaddamar da harin. Ya kira mu ta waya ya tabbatar da sace mutanen da ‘yan kungiyarsa suka yi.”

Ya kara da cewa, kwace sabbin babura guda biyu mallakin shugaban ‘yan ta’addan da jami’an tsaro suka yi a baya-bayan nan na iya jawo sace mutanen biyu.

Ya kuma bayyana cewa, sarkin ‘yan ta’addan ya kuma yi barazanar cewa tunda gwamnati ta san babura da jami’an tsaro suka kwace, wadanda abin ya shafa biyu a hannunsa za su fuskanci fushinsa.

Majiyar ta ce, suna bakin kokarinsu na ganin an sako wadanda aka sace cikin gaggawa, inda suka ce sun fara tattaunawa da sarkin domin tattaunawa kan yadda wadanda lamarin ya shafa za su samu ‘yancinsu.

Ba a samu damar jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Mohammed Shehu ta wayar tarho ba, domin jin ta bakinsa biyo bayan sace mutanen.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp