fidelitybank

An yi garkuwa da daliban jami’ar Abia

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun yi garkuwa da wasu daliban jami’ar jihar Abia, Uturu (ABSU) da ba a tantance adadinsu ba.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a ya fitar ta ce, lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:00 na daren ranar Alhamis.

An ce an yi garkuwa da daliban ne a kan titin Okigwe/Uturu, lokacin da motar bas din da suke ciki tare da wasu fasinjoji suka yi wa masu garkuwar kwanton bauna.

Biyu daga cikin wadanda abin ya shafa an ce daliban Jami’ar ne a fannin likitanci.

An bayyana cewa, wadanda suka sace daliban sun tuntubi iyalan daliban inda suka bukaci Naira miliyan 2 akan kowannen su.

Mahukuntan cibiyar, yayin da suke bayar da tabbacin cewa, a na kokarin ganin an sako su, sun shawarci daliban da su guji tafiye-tafiye da daddare.

Wani dalibi da ya yi magana kan lamarin, ya ce, abin takaici ne yadda duk da yawan shingayen binciken jami’an tsaro da ke kan titin Uturu/Okigwe mai tsawon kilomita biyar, har yanzu masu garkuwa da mutane na ci gaba da zama a yankin.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp