Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun yi garkuwa da wasu daliban jami’ar jihar Abia, Uturu (ABSU) da ba a tantance adadinsu ba.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a ya fitar ta ce, lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:00 na daren ranar Alhamis.
An ce an yi garkuwa da daliban ne a kan titin Okigwe/Uturu, lokacin da motar bas din da suke ciki tare da wasu fasinjoji suka yi wa masu garkuwar kwanton bauna.
Biyu daga cikin wadanda abin ya shafa an ce daliban Jami’ar ne a fannin likitanci.
An bayyana cewa, wadanda suka sace daliban sun tuntubi iyalan daliban inda suka bukaci Naira miliyan 2 akan kowannen su.
Mahukuntan cibiyar, yayin da suke bayar da tabbacin cewa, a na kokarin ganin an sako su, sun shawarci daliban da su guji tafiye-tafiye da daddare.
Wani dalibi da ya yi magana kan lamarin, ya ce, abin takaici ne yadda duk da yawan shingayen binciken jami’an tsaro da ke kan titin Uturu/Okigwe mai tsawon kilomita biyar, har yanzu masu garkuwa da mutane na ci gaba da zama a yankin.