fidelitybank

An yi garkuwa da Basarake Kogi

Date:

Wasu ƴanbidga sun kai hari garin Okoloke da ke ƙaramar hukumar Yagba ta yamma a jihar ta Kogi, inda suka kashe aƙalla mutum uku are da jikkata wasu da dama.

Maharan sun kuma yi garkuwa da babban basaraken al’ummar ta Okoloke, Pa Dada James Ogunyanda, a lokacin da ake tsaka da zaman fadanci, wanda bayanai suka tabbatar da cewa ba shi da cikakkiyar lafiya kuma yana daf da tafiya neman magani, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

‘Yan bindigar sun kuma kashe ƴanbanga biyu da wani ma’aikacin kamfanin sadarwa da ke aikin gyaran ƙarfen samar da sabis a yankin.

Rahotanni sun ce ‘yan bangar na samar wa ma’aikacin sadarwar tsaro ne lokacin da maharan suka yi musu kwanton ɓauna inda suka buɗe musu wuta nan take.

Hare-haren ‘yan bindiga dai na ci aba da ƙaruwa a baya-bayan nan musamman a jahohin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya da ma shiyar arewa maso gabashin Najeriya. Waɗanda ke kashe mutane da garkuwa da wasu domin neman kuɗin fansa.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp