Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi wata ganawar sirri tare da takwaransa na Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman, a ranar Lahadi, 27 ga watan Fabrairu.
Ganawar wacce ta shafe fiye da awa daya da rabi, daga 12.30 zuwa 2:05 na rana ya gudana ne a fadar sarkin Katsina, in ji Daily Trust.
Sai dai babu cikakken bayani kan ganawar tasu a daidai lokacin kawo wannan rahoton, amma akwai hasashen cewa, ba zai rasa nasaba da shigowar majalisar kolin Musulunci cikin batun murabus din Wazirin Katsina, Farfesa Sani Abubakar Lugga.
A takardar da yake martani ga tuhumar da aka masa, Farfesan ya amsa lamura uku da majalisar ke tuhumarsa a kai sannan daga bisani ya gabatarwa Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman takardarsa ta ajiye sarautarsa.