Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta sanar da fitar da sakamakon jarabawar gama gari ta shekarar 2025.
Hukumar ta bayyana cewa an hana sakamakon masu rubuta jarabawar 39,834.
Farfesa Ishaq Oloyede, magatakardar JAMB ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da ake fitar da sakamakon jarabawar UTME na shekarar 2025 a hukumance a hedkwatar JAMB, Bwari.
Oloyede ya bayyana cewa an kama sakamakon sakamakon da ake zargin an tafka magudin jarrabawa.
Ya kuma bayyana cewa kimanin mutane 80 ne ake binciken laifukan da suka shafi jarabawa, inda jihar Anambra ke da yawan wadanda ake zargi.