l’ummar Ogbese da ke karamar hukumar Akure ta Arewa a Jihar Ondo, ta shiga cikin tashin hankali, bayan wani kazamin rikici da ya barke tsakanin Fulani da Hausawa mazauna yankin.
An ce mutum daya ya mutu a rikicin tare da jikkata mutane da dama tare da lalata dukiyoyi.
An tattaro cewa rikicin da ya faro tun a yammacin ranar Talata ya yi kamari ne da safiyar Laraba, inda aka kona wasu shaguna na ‘yan Arewa a babbar kasuwar al’umma.
A lokacin da aka gabatar da wannan rahoto, har yanzu ba a san ainihin dalilin da ya haddasa rikicin ba, amma an gano cewa unguwar na cikin tashin hankali.
Sai dai wani dan unguwar ya yi ikirarin cewa rikicin ya samo asali ne daga wata hatsaniya tsakanin wani Bafulatani da ke zaune a dajin da kuma wani Bahaushe da ke zaune a unguwar a kan tabar wiwi da aka fi sani da hemp Indiya.
Kakakin ‘yan sandan, Funmilayo Odunlami, ta tabbatar da cewa shaguna 8 ne aka kone, amma ta musanta rahoton rikicin kabilanci.