fidelitybank

An yi dauki ba dadi tsakanin ‘yan ta’adda da kungiyar Ansaru a jihar Kaduna

Date:

An samu tashin hankali a karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna, yayin da wasu ‘yan bindiga da ‘yan ta’addan Ansaru suka yi artabu da bindiga.

‘Yan kungiyar Ansaru dai na yin wa’azi ga jama’ar yankin ne a lokacin da ‘yan bindigar suka far wa jama’ar, inda suka rika harbe-harbe ba da jimawa ba, inda suka kashe mutanen kauyen biyu.

Lamarin dai kamar yadda aka bayyana wa Aminiya ya ce, ‘yan bindigar sun shiga kauyen Damari da ke karkashin gundumar Kazage da ke yankin Gabashin karamar hukumar da nufin fatattakar ‘yan ta’addan daga kauyen.

An tattaro cewa, kungiyar Ansaru ta kwace yankuna da dama a Gabashin karamar hukumar da sunan jagorantar hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake tofa albarkacin bakinsa, Shugaban kungiyar cigaban Masarautar Birnin-Gwari (BEPU), Ishaq Usman Kafai, ya shaidawa manema labarai cewa, an dauki tsawon sa’a guda ana rikicin tsakanin kungiyoyin biyu.

A cewarsa, ‘yan kungiyar ta Ansaru wadanda su ma dauke da muggan makamai sun yi galaba a kan ‘yan bindigar wanda hakan ya sanya su ‘yan bindigar suka koma kauyen.

Duk da haka, a cewar Kafai, an samu asarar rayuka da dama yayin arangamar.

“An samu barna a yayin arangamar; an kona wani shago; motoci biyu sun kone; An kona wani Asibiti mai zaman kansa. ‘Yan bindigar ma sun kashe wasu ‘yan unguwar (ma’aikata) guda biyu yayin da ‘yan fashin ke guduwa cikin dajin,” inji shi.

Ishaq ya shaidawa kafar yada labarai cewa asibitin ya kone bisa kuskure sakamakon gobarar da ta tashi daga wata mota da ta kone.

Ya kara da cewa, ba a iya tantance adadin da aka kashe tsakanin ‘yan bindigar da ‘yan Ansaru ba amma ya ce mutanen yankin sun yaba wa ‘yan kungiyar ta Ansaru saboda kare garin daga harin ‘yan bindigar.

Naija News ta samu cewa daruruwan mazauna garin da suka hada da mata da kananan yara sun tsere daga garin yayin harin.

Rahoton ya ce ‘yan kungiyar ta Ansaru sun ci gaba da wa’azin bayan fafatawar inda suka shawarci jama’a da su mallaki makamai don kare kansu daga makiya tare da yaki da gwamnati domin tabbatar da abin da suke kira daular Musulunci.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp