fidelitybank

An yi dauki ba dadi a Kaduna da mabiya shi’a

Date:

An shiga ruɗani a Kaduna bayan da ƴan sanda suka yi kokarin tarwatsa mambobin kungiyar Islamic Movement Of Nigeria wadanda aka fi sani da ‘yan Shia, wadanda ke gudanar da muzahara a tsakiyar birnin.

Mambobin kungiyar sun taru a kan shatale-talen Katsina a Ahmadu Bello Way kafin ‘yan sanda su zo da kuma kokarin tarwatsa su.

Hakan ya janyo fargaba tsakanin mazauna birnin musamman ma wadanda suke da shaguna a kusa da hanyar.

An ruwaito cewa da dama daga ciki sun rufe shagunansu saboda tsoron abin da zai faru.

‘Yan sanda a Kaduna sun ce tattakin mambobin ‘yan Shiar na yau yana a matsayin haramtacce.

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar ASP Mansir Hassan, ya fada wa gidan talabijin na Channels cewa mambobin kungiyar sun fito da sanyin safiyar yau rike da makamai, inda suka fara far wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da sunan tattaki.

Mansir ya ce mambobin kungiyar sun far wa ‘yan sanda lokacin da suka yi kokarin tarwatsa su, inda ya ce har ta kai wasu daga cikin jami’ansu sun jikkata.

Ya ce an kama wasu daga ciki da ake zargi da rike muggan makamai kuma za a gurfanar da su gaban kotu idan aka kammala bincike.

Wanan dai ba shi ne karo na farko ba da ‘yan Shia ke gudanar da muzahara duk da haramta musu hakan da gwamnatin tarayya ta yi karkashin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari. In ji BBC.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp