Wasu ‘yan ta’adda da ke da alaka da kungiyar IS sun kashe sojoji shida a wani samame da suka kai a wani sansanin soji da ke arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda wasu majiyoyin soja biyu suka tabbatar wa kamfanin dillancin labaran Faransa a ranar Litinin.
Harin dai ya faru ne da sanyin safiyar Lahadin da ta gabata, lokacin da mayakan kungiyar IS da ke yankin yammacin Afirka (ISWAP) suka kaddamar da farmakin hadin gwiwa a sansanin da ke Sabon Gari, da ke gundumar Damboa a jihar Borno.
Majiyar sojojin ta bayyana cewa mayakan sun iso ne a cikin manyan motoci da babura, inda suka nemi a sakaya sunansu.
Majiyar ta kara da cewa maharan sun kona sansanin tare da lalata motocin sojoji a yayin farmakin.
“Mun rasa sojoji shida a harin da ‘yan ta’addar ISWAP suka kai a sansanin bayan wani kazamin fadan bindigu,” in ji wani jami’in soji, wanda ke bayyana mummunan fadan.
Daga karshe dai an tilastawa sojojin ja da baya, a cewar jami’in.
A wani mataki na mayar da martani, an jibge jiragen yaki daga babban birnin yankin, Maiduguri, mai tazarar kilomita 100 (kilomita 62) inda suka far wa mayakan da suka koma baya.
Jami’in soja na biyu, wanda ya bayar da adadin wadanda suka mutu, ya ce, “Harin da jiragen yaki suka kai kan ‘yan ta’addan da suka tsere ya yi sanadin asarar rayukan ‘yan bindiga da dama tare da lalata motocin da suke aiki da makamansu.”
Sai dai jami’in bai bayar da cikakken bayani kan adadin wadanda ISWAP ta kashe ba.