Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya ta ce gwamantin tarayya ta yi asarar kuɗi kimanin naira miliyan 113 sakamakon dakatar da jirgin ƙasan Abuja zuwa ƙaduna na tsowan wata takwas.
Babban daraktan hukumar Fidet Okhiria ne ya bayyana haka ga kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN.
Ya ƙara da cewa wasu ma da yawa daga cikin ɗaiɗaikun ‘yan ƙasar asarar ta shafe su sakamakon tsaida zirga-zirgar jirgin.
“Akwai mutanen da ke sayar da kayayyaki a cikin jirgin, akwai masu sana’o’i daban-daban a tasoshin jiragen, kuma mutane suna sayen abubuwa a wajensu”, in ji shi.