Akalla Falasdianwa 12 ne suka jikkata a masallacin Kudus a wani sabon rikici da ‘yan sandan Isra’ila da sanyin safiyar wannan Juma’ar.
Jami’an tsaro sun rinka jefa hayaki mai sa kwalla da harba harsasan roba domin tarwatsa masu zanga-zanga.
A cewarsu sun dauki wannan mataki ne ganin yadda Falasdinawa ke ta jifa da duwatsu da abubuwan wuta – akasari a bangon da Yahudawa ke gudanar da addu’o’insu.
Kuma a wannan lokacin ma ‘yan sandan Isra’ila sun ce sun shirya tunkarar dubban Falasdinawa da ake sa ran za su je sallah Juma’a yau a Masallacin.