fidelitybank

An wanke Sojojin Najeriya daga zargin tilasta wa Mata dubu 10 su zubar da ciki

Date:

Kwamitin bincike na Hukumar kare haƙƙin bil-adama ta Najeriya, NHRC ya kafa ya wanke sojojin Najeriya bisa zarginsu da tilasta zubar da cikin mata aƙalla 10,000 a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Shugaban kwamitin binciken, Abdul Aboki – wanda tsohon alƙalin kotun ƙolin ƙasar ne, tare da sauran mambobin bakwai, sun bayyana zargin da cewa ”ƙarya ce maras tushe” da ke cikin wani rahoto na musamman da wata kafar yaɗa labaran ƙasar waje ta wallafa.

A zaman ƙarshe da kwamitin ya yi ranar Juma’a a Abuja, ya ce babu wata hujja da ke tabbatar da wannan zargi da ke ƙunshe cikin rahoton.

“Dangane da batun tilasta zubar da ciki, kwamitin bai samu wata hujja da ke nuna cewa sojojin Najeriya sun aikata abin da ake zargnsu da shi na tilasta zubar da ciki a asirce na kusan mata 10,000 a yankin arewa maso gabas, babu wata hujja da ta nuna hakan a iya binciken da muka yi,” kamar yadda babban sakataren hukumar NHRC, Tony Ojukwu ya bayyana.

A watan Disamban 2022 ne kamfanin dillancin labarai na Reuters cikin wani rahotonsa ya zargi sojojin Najeriya da aikata laifukan keta haƙƙin bil-adama – ciki har da zargin tilasta wa mata da ‘yan mata aƙalla 10,000 zubar da ciki – a lokacin da suke yaƙi da ƙungiyar Boko Haram a arewa maso gabas tun 2013.

Rahoton ya ce an zubar da cikin ne ba tare da so ko izinin matan ba.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp