fidelitybank

An wanke Sojojin Najeriya daga zargin tilasta wa Mata dubu 10 su zubar da ciki

Date:

Kwamitin bincike na Hukumar kare haƙƙin bil-adama ta Najeriya, NHRC ya kafa ya wanke sojojin Najeriya bisa zarginsu da tilasta zubar da cikin mata aƙalla 10,000 a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Shugaban kwamitin binciken, Abdul Aboki – wanda tsohon alƙalin kotun ƙolin ƙasar ne, tare da sauran mambobin bakwai, sun bayyana zargin da cewa ”ƙarya ce maras tushe” da ke cikin wani rahoto na musamman da wata kafar yaɗa labaran ƙasar waje ta wallafa.

A zaman ƙarshe da kwamitin ya yi ranar Juma’a a Abuja, ya ce babu wata hujja da ke tabbatar da wannan zargi da ke ƙunshe cikin rahoton.

“Dangane da batun tilasta zubar da ciki, kwamitin bai samu wata hujja da ke nuna cewa sojojin Najeriya sun aikata abin da ake zargnsu da shi na tilasta zubar da ciki a asirce na kusan mata 10,000 a yankin arewa maso gabas, babu wata hujja da ta nuna hakan a iya binciken da muka yi,” kamar yadda babban sakataren hukumar NHRC, Tony Ojukwu ya bayyana.

A watan Disamban 2022 ne kamfanin dillancin labarai na Reuters cikin wani rahotonsa ya zargi sojojin Najeriya da aikata laifukan keta haƙƙin bil-adama – ciki har da zargin tilasta wa mata da ‘yan mata aƙalla 10,000 zubar da ciki – a lokacin da suke yaƙi da ƙungiyar Boko Haram a arewa maso gabas tun 2013.

Rahoton ya ce an zubar da cikin ne ba tare da so ko izinin matan ba.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp