Rotimi Amaechi ya kafa wani kwamiti da ya yi bincike a kan wa’adin Hadiza Bala Usman a NPA.
Kwamitin Ministan bai samu Bala Usman da laifin satar Naira Biliyan 165 daga asusun hukumar ba.
Binciken da aka yi ya nuna tsohuwar shugabar NPA ba ta ci kudi ba, amma ta rika sabawa Minista.
Rahoton The Cable ya bayyana cewa, an wanke tsohuwar shugabar hukumar NPA ta kasa, Hadiza Bala Usman, daga zargin satar kudi Naira Biliyan 165.
Zargin da ake yi wa Miss Hadiza Bala Usman na kin dawo da rarar biliyoyin da hukumar NPA ta samu cikin asusun gwamnatin tarayya, bai da madagora a doka.
Jaridar ta fitar da rahoto a ranar Talata, 15 ga watan Fubrairu 2022, ta ce kwamitin mutane 11 da Ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya kafa ya kammala aikinsa.