An samu akalla gawar mutum 10 a ƙauyen Unguwar Wakili da ke cikin ƙaramar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna, bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai wa ƙauyen hare.
A wata sanarwar da hukumomin ƙaramar hukumar suka fitar sun bayyana sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a ƙauyukan Ungwan Juju da Mabuhu da Ungwan Wakili da kuma garin Zango.
Karanta Wannan: Abun takaici ne ‘yan takara su yi amfani da addini da kabilanci a Kaduna – Hunkuyi
Sanarwar da mai taimaka wa shugaban ƙaramar hukumar kan harkokin yaɗa labarai Yabo Chris Ephraim, ya sanya wa hannu ta ce an sanya dokar hana fitar ne domin bai wa jami’an tsaro damar maido da zaman lafiya a yankunan.
Jihar Kaduna dai na ɗaya daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga.