fidelitybank

An tsinci gawar dan majalisar jihar Anambra bayan an yi garkuwa da shi

Date:

An tsinci gawar ɗan majalisar jihar Anambra, Justice Azuka mai wakiltar ƙaramar hukumar Onitsha ta Arewa, gunduma ta farko.

Gidan talbijin na Channels ya ruwaito cewa haɗin gwiwar jami’asn tsaron ƙasar ne suka gano gawar a gadar 2nd Niger Bridge.

A watan Disamban da ya gabata ne aka sace ɗan majalisar a birnin Onitsha.

Bayan shafe makonni ana bincike jami’an tsaro daga Abuja, suka kama wasu mutane da ake zargi da sace ɗan majalisar, inda suka kai jami’an har inda suka jefar da gawar Mista Azuka.

Wannan shi ne karo na biyu da ake sace ɗan majalisar jihar Anambra kuma a kashe shi a shekarun baya-bayan nan.

A shekarar 2022 ma an sace wani ɗan majalisa mai suna Okey Okoye, inda daga baya kuma aka kashe shi a wani yanki na jihar.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp