An gano gawar wani ɗan jaridar Kamaru bayan ɓacewarsa tun ranar Talata da ta gabata. An yi zargin cewa wasu ne suka yi garkuwa da shi.
Ɗan jaridar mai suna Martinez Zogo, ya kasance darektan wata gidan rediyo mai zaman kanta inda yake gabatar da wani shiri kan dokokin hanya.
A baya-bayan nan ya yi magana a kafar ƴada labarun kan batun zargin sama da faɗi da kuɗaɗe da ake yi wa manyan ƴan kasuwa da kuma jami’an gwamnati.
Wani mai magana da yawun gidan rediyon tare da matarsa, sun ce sun gani gawar ɗan jaridar a wani wuri a wajen Yaoundé, babban birnin ƙasar.
Wani mai fafutukar kare hakkin ‘yan jarida, ya ce ya jiyo hayaniya ta ‘yan sanda a wajen tashar a daren Talata, inda aka gano motarsa da aka lalata.
An kuma gano wata bakar mota na wucewa ta wajen da lamarin ya faru.