fidelitybank

An tsige Lamidon Adamawa daga shugaban majalisar Sarakuna

Date:

Majalisar dokokin jihar Adamawa, ta amince da ƙudurin kafa wasu masarautu uku masu daraja ta ɗaya a jihar.

Dokar, wadda yanzu take jiran sa hannun gwamnan jihar, Ahmadu Finitiri, na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnan ya sa hannu kan wata dokar ta ƙirƙirar gundumomi 84 a 4 ga Disamba.

A wata wasiƙa da gwamna da aika majalisar, ya buƙace su da su amince da ƙudurin naɗawa da cire sarakuna na jihar, wadda za ta ba gwamnan damar ƙirƙirar sababbin masarautu, naɗa sarakuna da cire su, kamar yadda muka kalato daga jaridar Premium Times.

Ƙudurin ya tsallake karatu na farko da na biyu a majalisar a ranar Litinin, sannan a ranar Talata ƴanmajalisar suka amince da shi, inda yanzu ake jiran sa hannun gwamna domin ya zama doka.

Sabuwar dokar, ta cire wa Lamiɗon Adamawa, Mustapha Barkindo, muƙaminsa na shugaban majalisar sarakunan Adamawa na dindindin, inda yanzu zai riƙa zagawa da matsayin tsakanin sarakunan jihar masu daraja ta ɗaya.

Sannan a dokar ta farko da gwamnan ya sa hannu, an rage ƙasar Lamidon Adamawa daga ƙananan hukumomi takwas zuwa uku.

A baya, ƙananan hukumomin Hong, Song, Gombi, Fufore, Girei, Yola ta arewa, Yola da kudu, da Mayo-Belwa suna ƙarƙashin masarautar Adamawa ne, amma yanzu Girei, Jimeta da Yola ne kawai suke ƙarƙashin masarautar.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp