fidelitybank

An tsige Lamidon Adamawa daga shugaban majalisar Sarakuna

Date:

Majalisar dokokin jihar Adamawa, ta amince da ƙudurin kafa wasu masarautu uku masu daraja ta ɗaya a jihar.

Dokar, wadda yanzu take jiran sa hannun gwamnan jihar, Ahmadu Finitiri, na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnan ya sa hannu kan wata dokar ta ƙirƙirar gundumomi 84 a 4 ga Disamba.

A wata wasiƙa da gwamna da aika majalisar, ya buƙace su da su amince da ƙudurin naɗawa da cire sarakuna na jihar, wadda za ta ba gwamnan damar ƙirƙirar sababbin masarautu, naɗa sarakuna da cire su, kamar yadda muka kalato daga jaridar Premium Times.

Ƙudurin ya tsallake karatu na farko da na biyu a majalisar a ranar Litinin, sannan a ranar Talata ƴanmajalisar suka amince da shi, inda yanzu ake jiran sa hannun gwamna domin ya zama doka.

Sabuwar dokar, ta cire wa Lamiɗon Adamawa, Mustapha Barkindo, muƙaminsa na shugaban majalisar sarakunan Adamawa na dindindin, inda yanzu zai riƙa zagawa da matsayin tsakanin sarakunan jihar masu daraja ta ɗaya.

Sannan a dokar ta farko da gwamnan ya sa hannu, an rage ƙasar Lamidon Adamawa daga ƙananan hukumomi takwas zuwa uku.

A baya, ƙananan hukumomin Hong, Song, Gombi, Fufore, Girei, Yola ta arewa, Yola da kudu, da Mayo-Belwa suna ƙarƙashin masarautar Adamawa ne, amma yanzu Girei, Jimeta da Yola ne kawai suke ƙarƙashin masarautar.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp