Majalisar dokokin jihar Adamawa, ta amince da ƙudurin kafa wasu masarautu uku masu daraja ta ɗaya a jihar.
Dokar, wadda yanzu take jiran sa hannun gwamnan jihar, Ahmadu Finitiri, na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnan ya sa hannu kan wata dokar ta ƙirƙirar gundumomi 84 a 4 ga Disamba.
A wata wasiƙa da gwamna da aika majalisar, ya buƙace su da su amince da ƙudurin naɗawa da cire sarakuna na jihar, wadda za ta ba gwamnan damar ƙirƙirar sababbin masarautu, naɗa sarakuna da cire su, kamar yadda muka kalato daga jaridar Premium Times.
Ƙudurin ya tsallake karatu na farko da na biyu a majalisar a ranar Litinin, sannan a ranar Talata ƴanmajalisar suka amince da shi, inda yanzu ake jiran sa hannun gwamna domin ya zama doka.
Sabuwar dokar, ta cire wa Lamiɗon Adamawa, Mustapha Barkindo, muƙaminsa na shugaban majalisar sarakunan Adamawa na dindindin, inda yanzu zai riƙa zagawa da matsayin tsakanin sarakunan jihar masu daraja ta ɗaya.
Sannan a dokar ta farko da gwamnan ya sa hannu, an rage ƙasar Lamidon Adamawa daga ƙananan hukumomi takwas zuwa uku.
A baya, ƙananan hukumomin Hong, Song, Gombi, Fufore, Girei, Yola ta arewa, Yola da kudu, da Mayo-Belwa suna ƙarƙashin masarautar Adamawa ne, amma yanzu Girei, Jimeta da Yola ne kawai suke ƙarƙashin masarautar.