A ranar 6 ga watan Mayu ne za a gudanar da zaɓen shugaban kasar Chadi, wanda zai kawo karshen mulkin soji na shekaru uku da aka soma bayan shugaba Mahamat Idriss Deby Itno ya hau ƙaragar mulki bayan rasuwar mahaifinsa a shekarar 2021.
Shugaban hukumar zaɓen kasar Ahmed Bartchiret, ya bayyana muhimman ranakun da za a gudanar da zaben shugaban kasar a lokacin da yake ganawa da manema labarai a babban birnin kasar, N’Djamena, kamar yadda shafin intanet na Tchadinfos mai zaman kansa ya ruwaito.
Bartchiret ya jaddada muhimmancin gudanar da zaɓen kafin lokacin damina, inda ya buƙaci abokan huldar fasaha da na kudi da su ba da hadin kai ga shirin zaɓen kasar.
Yayin da har yanzu shugaba Deby bai bayyana sake tsayawa takara ba a hukumance, ‘yan adawa sun buƙaci da kada ya sake neman wani wa’adi
Deby, mai shekaru 38, ya yi alkawarin shirya zaɓuka cikin watanni 18 bayan ya ɗare kan ƙaragar mulki a watan Afrilun 2021.
Duk da haka, gwamnatinsa ta soji ta ci gaba da riƙe madafun iko, inda ta ƙara wa’adin mulkinta da ƙarin watanni 18.