A ranar Asabar ne 11 ga watan Nuwamba, al’ummar jihar Kogi za su fita rumfunan zaɓar sabon gwamna.
Gwamna Yahaya Bello na jihar na kammala wa’adin mulkinsa na shekara takwas, inda ƴan takara 18 ke ƙoƙarin gadarsa.
Gabanin zaɓen, an jibge jami’an tsaro da dama don tabbatar da an gudanar da zaɓen lami lafiya.