fidelitybank

An tsaurara tsaro gabanin fara sauraron shari’ar Gwamnan Nasara

Date:

An saka tsauraran matakan tsaro a harabar kotun daukaka kara da ke Abuja yayin da kotun za ta yanke hukunci a shari’ar zaben gwamnan jihar Nasarawa.

Jami’an tsaro dauke da muggan makamai daga rundunar ‘yan sandan Najeriya, da hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, da kuma jami’an tsaron farin kaya sun killace dukkanin hanyoyin da ke zuwa kotun daukaka kara.

Motoci masu zaman kansu da na ‘yan kasuwa da ke bin hanyoyin sakatariyar gwamnatin tarayya zuwa wurare daban-daban, an karkatar da su zuwa wasu hanyoyin tare da jami’an hukumar kiyaye hadurra ta kasa FRSC, inda suka yi ta gwabzawa domin shawo kan cunkoson ababen hawa da suka samu kan hanyar.

Mahukuntan kotun ne suka aiwatar da matakan tsaron, kamar yadda jaridar DAILY POST ta tattaro, domin dakile yiwuwar karya doka bayan yanke hukunci.

Har zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoto, duka ma’aikatan kotun, lauyoyi, masu kara da kuma manema labarai suna ta kutsawa cikin babbar kofar shiga harabar kotun.

Duk da cewa an amince da wasu ‘yan jarida da dama da suka bayar da labarin yadda aka yanke hukuncin, biyar daga cikinsu ne kawai aka ba su damar shiga cikin dakin kotun saboda abin da wani jami’in kotun ya dorawa laifin rashin isasshen kujeru da kuma kula da jama’a.

Wakilinmu ya lura da cewa wasu daga cikin jami’an jam’iyyar siyasa da aka amince da su da masu goyon bayansu da suka isa kotun tun da karfe 8 na safe ne aka ba su izinin shiga harabar kotun, yayin da wasu da dama kuma ‘yan sandan tafi da gidanka dauke da makamai suka hana su zuwa nesa.

An dai gwabza kazamin fada tsakanin gwamna mai ci a jihar Abdullahi Sule na jam’iyyar APC da abokin hamayyarsa David Ombugadu na jam’iyyar PDP.

Idan dai ba a manta ba, kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Nasarawa ta yanke hukunci mai rinjaye na biyu zuwa daya ta soke zaben gwamna Sule saboda rashin samun rinjayen kuri’un da aka kada a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Kotun ta bayyana Ombugadu, tsohon dan majalisar wakilai a matsayin wanda ya lashe zaben bisa ka’ida.

A halin yanzu dai ana dakon alkalai domin yanke hukunci.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp