fidelitybank

An tsare ɗan ƙasar Saudiyya a Jamus bayan zargin ya murƙushe mutane har lahira

Date:

Wani alƙali a birnin Magdeburg na ƙasar Jamus ya bayar da umarnin tsare wani ɗan ƙasar Saudiyyan da aka kama bisa zargin kai mummunan hari kan wata kasuwar Kirsimeti a birnin.

An gabatar da mutumin mai shekara 50 a gaban alƙali da maraicen ranar Asabar, bisa zargin tuƙo mota tare da kutsawa cikin kasuwar mai cike da cunkoson jama’a.

A wani taron manema labarai, mai gabatar da ƙara a birnin na Magdeburg, Horst Walter Nopens ya ce maharin shi kaɗai ya kitsa ya kuma kai harin.

Ya ce saɓanin rahotannin da ke ta yawo a shafukan sada zumunta a jiya, mai laifin mutum guda ne, kuma babu alamun akwai wani da ke aiki tare da shi.

Aƙalla mutum biyar ne suka mutu, da suka haɗa da mata uku da wani yaro mai shekara tara, yayin da sama da 200 suka jikkata a harin da aka kai da yammacin ranar Juma’a.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp