fidelitybank

An tsare ɗan ƙasar Saudiyya a Jamus bayan zargin ya murƙushe mutane har lahira

Date:

Wani alƙali a birnin Magdeburg na ƙasar Jamus ya bayar da umarnin tsare wani ɗan ƙasar Saudiyyan da aka kama bisa zargin kai mummunan hari kan wata kasuwar Kirsimeti a birnin.

An gabatar da mutumin mai shekara 50 a gaban alƙali da maraicen ranar Asabar, bisa zargin tuƙo mota tare da kutsawa cikin kasuwar mai cike da cunkoson jama’a.

A wani taron manema labarai, mai gabatar da ƙara a birnin na Magdeburg, Horst Walter Nopens ya ce maharin shi kaɗai ya kitsa ya kuma kai harin.

Ya ce saɓanin rahotannin da ke ta yawo a shafukan sada zumunta a jiya, mai laifin mutum guda ne, kuma babu alamun akwai wani da ke aiki tare da shi.

Aƙalla mutum biyar ne suka mutu, da suka haɗa da mata uku da wani yaro mai shekara tara, yayin da sama da 200 suka jikkata a harin da aka kai da yammacin ranar Juma’a.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp