fidelitybank

An tsamo gawarwaki 18 yayin da kwale-kwale ya kife da ‘yan yawon bikin Sallah

Date:

Akalla gawarwaki 18 ne aka gano yayin da wasu mutane shida suka bata, bayan da wani kwale-kwale ya kife a karamar hukumar Mai’adua ta jihar Katsina.

Wani mazaunin garin, Lawal Sakatare, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mutane 24 da suke cikin jirgin yayin zuwa bikin Sallah a lokacin da ya kife, kuma mutane 18 wadanda yawancinsu kananan yara ne suka nutse.

ā€œSha hudu daga cikinsu ā€˜yan kauyen Tsabu ne, hudu kuma ā€˜yan kauyen Dogon Hawa ne. An yi jana’izar 15 daga cikin 18 a Mai’adua a yau (Alhamis) yayin da sauran mutane shida da ke cikin jirgin suka bace,ā€ inji shi.

Ya kara da cewa, tawagar da ta fito daga kauyukan da lamarin ya shafa na ci gaba da aikin ceto sauran shidan, duk da cewa fatan samun su da rai ya dushe.

Kakakin rundunar ā€˜yan sandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, bai amsa kiran da aka yi masa ba a cewar Daily Trust, ko kuma ya amsa sakon tes da aka aike domin neman jin ta bakinsa kan lamarin.

A wani labarin kuma, wata motar jami’an hukumar kwastam dake fafatawa da wasu da ake zargin masu fasa kwaurin ne a karamar hukumar Jibia ta Katsina ta murkushe mutum daya a ranar Laraba.

Wasu uku kuma sun samu raunuka a lamarin.

An bayyana cewa marigayin yana kan hanyarsa ta zuwa Katsina daga Jibia a kan babur, sai motar da ke gudu mai tsananin gudu ta farfasa shi.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp