fidelitybank

An toshe Facebook da Whatsapp a Senegal

Date:

Hukumomi a Senegal sun toshe hanyoyin shiga shafukan sada zumunta da muhawara da suka hada da Facebook da WhatsApp sakamakon kazamin rikicin da ya biyo bayan hukuncin daurin shekara biyu da kotu ta yanke wa jagoran ‘yan hamayya na kasar.

Daman gwamnatin ta ce za ta dau duk wani mataki da ya dace domin kare rayuwar al’umma da dukiyoyi bayan mutuwar mutane sakamakon rikicin.

Akalla mutum tara ne suka mutu a rikici tsakanin ‘yan sanda da masu zanga-zanga, bayan yanke wa Ousmane Sanko hukuncin a jiya Alhamis.

Ministan cikin gida, Antoine Diome a wani taron ‘yan jarida a cikin dare, ya ce an toshe kafofin ne, yana mai nuna takaicin abubuwan da suka faru.

Rikicin ya fi baci a yankin Ziguinchor – (Zi-gan-shiyo)- da ke kudancin kasar, inda Mista Sonko ke rike da mukamin magajin gari.

Hukukuncin kotun da aka yanke a bayan idonsa na iya hana shi tsayawa takarar shugaban kasa a zaɓen shekara mai zuwa.

An same shi da laifin nuna rashin É—a’a, amma an wanke shi daga zargin aikata fyaÉ—e.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp