fidelitybank

An tiso ƙeyar Ƴan Nijar 600 daga Libiya

Date:

Mutum 600 ne suka isa garin Dirkou jihar Agadez.ta Nijar bayan mahukunta sun koro su daga ƙasar Libya.

Hukumomin Dirkou ne da abokan hulɗarsu na hukumar Majalisa Ɗinkin Duniya da ke kula da baƙin haure suka tarbe su.

Da yawansu sun yi zaman gidan yari na tsawon watanni a Libya ba tare da shari’a ba.

“Watana biyar a gidan kaso kafin a kawo mu Nijar,” in ji wani daga cikinsu. Wani ma ya ce: “Mun sha wahala sosai. Ƙuraje sun fito min, mun sha wahala sosai.”

A ranar 1 ga watan Janairu ma bakin haure kimanin 770 ne suka isa Nijar din.

Mutanen da suka yi ta aika saƙonnin neman taimako saboda mawuyacin halin da suka fada a gidan yarin Gatrone da dama sun koma gida ɗauke da larura, yayin da mutum ɗaya ya rasu.

Jimillar ‘yan Nijar 1,300 ne suka isa ƙasar bayan koro su daga Libya, a cewar wakiliyar BBC Tchima Illa Issoufou.

Wani jami’in barikin da ya karɓi mutanen, Abare Abba Gana, ya ce dukka mutanen maza ne.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp